✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Hatsarin mota ya yi ajalin mutum 19 a hanyar Kaduna-Abuja

Hatsaarin mota ya yi ajalin mutum 19 da ke kan hanyar zuwa Kano daga Legas.

Akalla matafiya 19 ne suka rasu a hanyar Kaduna zuwa Abuja a daren ranar Lahadi, sakamakon hatsari da ya ritsa da su a daidai garin Kateri.

Hatsarin ya faru ne da misalin karfe 8 na dare, kuma nan take mutum 16 suka rasu, uku kuma suka rasu a asibiti daga baya.

Hatsarin ya auku ne da wata babbar mota kirar DAF, wadda ta taso daga Legas zuwa Kano, dauke da fasinja 53.

Da yake tabbatar da faruwar hadarin, Kwamandan Hukumar Kiyaye Hadura FRSC reshen Jihar Kaduna, Hafiz Mohammed, ya sce mutum 19 sun mutu, yayin da 34 suka ji rauni daga cikin mutum 53 da ke cikin motar.

Ya kara da cewa an ajiye gawarwakin a dakin ajiye gawa na Babban Asibitin garin Doka da ke kan hanyar Kaduna-Abuja.

Sannan ya ce ’yan uwan wanda suka rasun, tuni suka fara zuwa daukar gawarwakin ’yan uwan nasu, wanda yawancin daga Zariya da Kano suka fito.

Kwamishinan Tsaro da Harkokin Cikin Gida, Samuel Aruwan, ya ziyarci inda hadarin ya auku, inda ya ce gwamnan jihar, Nasir El-Rufai, ya nuna alhininsa game da wanda suka rasa rayukansu, tare da addu’ar kiyaye faruwar hakan.

Ya kuma yi ta’aziyyar ga iyalan wanda hadarin ya ritsa da su sannan ya ja hankalin direbobi da su kasance masu kiyaye ka’idojin tuki.