✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Hatsarin Mota ya yi ajalin mutum biyu a Kano

Gudun wuce kima ya yi sanadin ajalin wasu mutum biyu a kan hanyar Kano-Zariya.

Hukumar Kiyaye Hadura ta Kasa (FRSC), ta tabbatar da mutuwar mutane biyu, sannan biyar sun ji rauni a wani hadarin mota da ya ritsa da su a kauyen Dakatsalle da ke kan hanyar Kano zuwa Zariya.

Kwamandan Hukumar reshen Jihar Kano, Mista Zubairu Mato ne ya tabbatar da hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Litinin.

“Mun samu kiran neman agajin gaggawa da misalin karfe 3:15 na dare a ranar 29 ga Maris, 2021.

“Bayan samun kiran ne nan take muka aike da jami’anmu kuma suka isa wurin da hadarin ya auku don ceto mutane da misalin 3:40 na dare”, a cewar Mato.

“Hadarin ya ritsa da mutane maza 13 kuma daga ciki biyu sun rasa rayukansu, sannan wasu biyar sun jikkata,” a cewarsa.

Kwamandan, ya ce hadarin ya auku ne sakamakon gudun wuce kima tsakanin wata motar haya kirar Peugot 306 mai lamba TFA 429 da tirela mai lamba KTJ 574 XA.

Mato ya kara da cewa an garzaya da wanda suka samu raunuka zuwa babban asibitin garin Kura inda kuma aka mika gawawwakin wadanda suka rasu ga ‘yan uwansu.