✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Hisba ta kama barayin waya 8 a masallaci a Kano

Hisbah ta ce daga cikin mutanen har da maza da mata

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta bayyana kama mutum takwas maza da mata da take zargi da satar waya da sauran manyan laifuka a masallacin Al-Furqan da ke unguwar Nasarawa a Kano.

Babban Kwamandan hukumar na Kano, Harun Ibn Sina ne ya tabbatar da kama matasan ga ’yan jaridu ranar Talata.

Ya ce wadanda ake zargin an kama su ne da yamma yayin da suke shan kwaya da sauran kayan maye a kusa da masallacin.

Ibn Sina ya alakanta wannan dabi’a ta matasan a matsayin wacce ta sabawa addinin Musulunci, musamman a watan Ramadan.

A don haka yayi kira ga al’umma da su sa ido tare da kai rahoton duk wani wanda suka gami suke kuma zargi da aikata ba daidai ba ga hukumar.

Ya ce Hisbah ba za ta yi kasa a guiwa ba a aikinta na tsaftace Kano daga dukkan abin ki.

A karshe ya ce za su mika wadanda ake zargin ga hukumomin da suka dace domin daukar mataki.