✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Hisba ta kama mabarata 648 a Kano

Mata 416 ne da kuma maza 232 hukumar Hisbah ta kama a Kano

Hukumar Hisba ta Jihar Kano ta kama akalla mutum 648 da ake zargin mabarata ne a titunan daban-daban na garin Kano daga watan Fabrailu zuwa yanzu.

Mai magana da yawun hukumar, Lawan Ibrahim, ya ce wadanda ake zargin an kama su ne a titunan Bata da Murtala Muhmamed da Asibitin Nasarawa da hanyar jirgin kasa da kuma Titin Yahuza Suya a cikin garin Kano. Mata 416 ne da kuma maza 232 aka kama.

Ibrahim ya ce hukumar za ta ci gaba da kama masu bara da suka ki bin dokar hana bara da gwamnatin ta saka.

“Za mu tabbatar da hana bara a titunan Kano.

“An kuma tantance wadanda aka kama, haka kuma wanda aka samu laifinsu ne na farko za a mika su wajen ‘yan uwansu.

“Wadanda kuma suka saba yi za mu kai su kotu”, inji shi, kamar yadda kamfanin dillacin labarai na NAN ya ruwaito.