✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Hisbah ta kwace kwalaben giya 8,400 a Kano

’Yan Hisbah sun kwace kwalaben giya 8,400 a wata mota da ta shigo daga Kaduna

’Yan Hisba a Jihar Kano sun kwace kwalaben giya 8,400 a kananan hukumomin Dawakin Kudu da Kura da ke jihar.

Babban Kwamandan Hisbah a Jihar Kano, Harun Ibn-Sina, ya ce an kama giyar ce a wata mota da ta taho daga Zariya kuma jami’an hukumar sun kama direban motar.

“Hukumar Hisbah ta haramta sayar da giya a fadin jihar domin hana mutane yin maye”, inji Kwamandan.

Ibn-Sina ya ce da zarar Hukumar ta kammala bincike za a gurfanar da wadanda ake zargin a gaban kuliya.

Ya ce hukumar ta umarci jami’anta da su kara sa ido sosai domin tabbatar da hana shigar da haramtattun ababuwa cikin jihar.

Sannan ya bukaci jama’ar gari da su yi da’a ga dokar hana sha ko sayar da barasa kuma su tsegunta wa Hisba a duk lokacin da suka fahimci ana kokarin shigo da giya ko sauran kayan maye cikin jihar.