✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Hotuna: Gwamnonin da aka yi wa allurar rigakafin Coronavirus a Najeriya

A makon da ya shude ne aka yi wa Shugaba Muhammadu Buhari da Mataimakinsa Yemi Osinbajo allurar rigakafin cutar Coronavirus ta AstraZeneca wanda aka yada…

A makon da ya shude ne aka yi wa Shugaba Muhammadu Buhari da Mataimakinsa Yemi Osinbajo allurar rigakafin cutar Coronavirus ta AstraZeneca wanda aka yada a gidajen talabijin na kasar da kewaye.

Shugaban Kasar tare da mataimakinsa sun yi hakan ne domin kara wa al’ummar kasar karfin gwiwa da janyo hankulansu a kan muhimmancin karbar rigakafin cutar da ta zamto annoba ga duniya baki daya.

Kazalika, yunkurin masu rike da madafan ikon kasar na zuwa ne domin kawar da shakku dangane da rade-radin da ke yaduwa a kan amincin rigakafin.

Gwamna Yahaya Bello na Jihar Kogi, shi kadai ne gwamnan da ya fito karara ya nesanta kansa da rigakafin wanda a cewarsa mutanen jiharsa ba aladu ba ne da za a yi musu wata rigakafin da ba su yarda da ita ba ballantana ita kanta cutar.

Sai dai takwarorinsa da dama sun karbi rigakafin a bainar jama’a domin nuna amincinsu a kanta da kuma kara wa al’ummarsu kwarin gwiwa.

A kidayar da Aminiya ta gudanar, ta lura cewa a halin yanzu akalla gwamnonin jihohi 14 sun karbi rigakafin. Ga hotunansu:

Gwamna El-Rufai na Jihar Kaduna
Gwamna Rotimi Akeredolu na Jihar Ondo
Gwamna Kayode Fayemi na Jihar Ekiti
Gwamna Gboyega Oyetola na Jihar Osun
Gwamna Sani Bello na Jihar Neja
Gwamna Muhammad Badaru na Jihar Jigawa
Gwamna Okezie Ikpeazu na Abiya
Gwamna Ahmadu Fintiri na Jihar Adamawa
Gwamna Ifeanyi Okowa na Jihar Delta
Gwamna Babajide Sanwo-Olu na Jihar Legas
Gwamna Abdullahi Umar Ganduje na Jihar Kano
Gwamna Abdulrahman Abdulrazaq na Jihar Kwara
Gwamna Dapo Abiodun na Jihar Ogun
Gwamna Bala Muhammad na Jihar Bauchi