✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Ibrahim Attahiru: Tarihin Babban Hafsan Sojin Kasa na Najeriya

A watan Janairu ya zama Babban Hafsan Sojin Kasa na Najeriya.

A Juma’ar da ta gabata ce Allah Ya yi wa Babban Hafsan Sojin Kasa na Najeriya, Laftanar Janar Ibrahim Attahiru rasuwa a hatsarin jirgin sama.

Laftanar Janar Attahiru, wanda dan asalin Jihar Kaduna ne, ya zama Shugaban Rundunar Sojin Kasa ta Najeriya a ranar 26 ga Janairu, 2021.

Sai dai watanni hudu bayan kama aiki, hatsarin jirgin sama ya ritsa da shi a Filin Jirgin Sama na Kaduna, inda karar ta cimmai tare da wasu manya da kananan hafsoshin sojin kasar.

A ranar 10 ga watan Agustan 1966 aka haifi Marigayi Ibrahim Attahiru inda ya kammala Makarantar Horar da Hafsoshin Soji ta Nigerian Defence Academy (NDA) a 1986, bayan shigarsa a waan Janairun 1984.

Ya samu kwarewa a fagen aikin soji daga Armed Forces Command Staff College da ke Jaji da kuma Kwalejin da ke Horar da Kananan Hafsoshin Soji ta Nigerian Army School of Infantry dukkansu a Jihar Kaduna.

Ya ci gaba da karatu domin karo ilimi, inda ya samu shaidar digiri na biyu a Jami’ar Salford da ke Birtaniya, bayan wata babbar Diploma da ya samo a Jami’ar Nairobi da ke Kasar Kenya.

Marigayin shi ne ya maye gurbin Janar Tukur Yusuf Buratai, a matsayin Babban Hafsa Sojan Kasa na Najeriya.

Kafin samun wannan mukami, shi ne Shugaban runduna ta 82 a rundunar sojin kasar.

Sannan ya rike mukamai da dama a lokacin rayuwarsa, ciki har da Kwamandan rundunar Operation Lafiya Dole mai yaki da masu tayar da kayar baya a yankin Arewa-maso-Gabas.