✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Iheanacho da Ndidi sun taimaki Leicester ta lashe kofin Gasar FA

Leicester City ta lashe gasar FA a karon farko cikin shekaru 137 da kafa ta.

’Yan wasan Najeriya biyu, Kelechi Iheanacho da Wilfred Ndidi, sun taimaka wa kungiyar kwallon kafa ta Leicester City, wurin doke Chelsea da ci 0-1 a wasan karshe na gasar FA, na kasar Ingila.

Karo na farko ke nan da kungiyar Leicester City ta lashe gasar FA cikin shekaru 137, tun bayan kafa kungiyar.

Kwallom da dan wasa Youri Tielemans ya zura a gaban ’yan kallo mutum 22, 000 a filin wasa na Wembley, ita ce ta raba raini tsakanin kungiyoyin biyu.

‘Yan wasan Leicester City na murna, bayan zura kwallo a minti na 63.

Wannan shi ne karo na farko da aka samu ’yan kallo masu yawa a filin wasa a kasar Ingila, tun bayan barkewar annobar COVID-19.

Youri Tielemans, dan asalin kasar Belgium, ya zura kwallon ne a minti na 63, daga bugun kusurwa da kungiyar ta Leicester ta yi.