Rundunar ’Yan Sanda ta Jihar Imo ta ce matasa dauke da makamai sun tayar da bam a ofishin ’yan sanda na Njaba da ke Jihar inda suka lalata wani sashe na ginin.
Maharan dai mambobin haramtacciyar kungiyar ’yan awaren Biyafara ne ta IPOB ne.
- Makabartar Gombe da ake binne akalla jarirai 10 a kullum
- Yadda karyewar gada ta kashe mutum 18 a Kano
To sai dai ’yan sandan sun sami nasarar kashe biyu daga cikinsu tare da kwace motarsu, yayin da sauran suka tsere.
Kakakin rundunar a Jihar, CSP Mike Abatam a cikin wata sanarwar ranar Asabar ya ce an kai harin ne da misalin karfe 1:20 na daren ranar Asabar amma aka tarwatsasu.
A cewar sanarwar, yayin da ake bincikar motar tasu da aka kwace, an sami bindiga kirar AK-47 da kuma harsasai guda 10 da wata karamar bindiga kirar gida da kuma wata jigida guda daya.
“Sun kuma kwance wani bam da suka dana a kusa da ofishin ’yan sanda na Njaba amma sun yi ’yar karamar barna,” inji sanarwar.
Kakakin ya kuma ce sun kaddamar da bincike a yankin domin kama maharan da suka tsere.