✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

IPPIS: ASUU ta shiga ganawar sirri da jagororin Majalisar Dattawa

Ina dalilin da za ku kulla yarjejeniyar da kun san ba ku da ikon cika wa?

A halin yanzu, Kungiyar Malaman Jami’o’in Najeriya ta ASUU, ta shiga bayan labule tare da Jagororin Majalisar Dattawa.

ASUU da Shugabannin Majalisar na ganawa a kan rashin jituwar da ke tsakaninta da Gwamnatin Tarayya musamman dangane da tsarin biyan albashi na bai daya (IPPIS).

Gabanin kebancewar da suka yi inda aka nemi manema labarai su janye jiki, Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Ahmad Lawan, ya bayyana damuwarsa a kan yadda har kawo yanzu aka gaza cimma matsaya tsakanin Kungiyar Malaman da kuma Gwamnatin Tarayya.

Sanata Lawan yayin bayyana damuwa dangane da rashin cika alkawalin da Gwamnatin Tarayya ta rika yi wa Kungiyar ASUU a baya ya ce, “ina dalilin da za ku kulla yarjejeniyar da kun san ba ku da ikon cika wa?”

Shugaban ASUU Farfesa Biodun Ogunyemi wanda ya jagoranci tawagar kusoshin kungiyar, ya ce ganawar ta su za ta mayar da hankali wajen neman goyon bayan Majalisar Dattawa don tayi ruwa da tsaki wajen ganin Gwamnatin Tarayya ta amince da tsarin biyan albashin da suka kawo sabanin na IPPIS tun tsawon shekaru biyar da suka gabata.

Yayin gabatar da kasafin kudin badi ranar Alhamis a zauren Majalisar Dokoki ta Tarayya, Shugaba Muhammadu Buhari ya sanar cewa duk Ma’aikacin Gwamnatin Tarayya da bai shigar da bayanansa ba a tsarin IPPIS, ba zai sake samun albashi ba daga yanzu zuwa watan Nuwamba.