✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Jadawalin gasar cin Kofin Zakarun Turai

An hada PSG da Man City a rukuni daya.

Hukumar Kwallon Kafar Turai UEFA, ta fitar da sabon jadawalin gasar cin Kofin Zakarun Turai na kakar wasanni ta 2021/2022.

A yayin bikin fitar da jadawalin da aka gudanar ranar Alhamis a birnin Istanbul na kasar Taki, UEFA ta ce wasannin gasar za su fara daga 14 ga watan satumba mai kamawa zuwa ranar 28 watan Mayun 2022.

A rukunin farko na jadawalin wato rukunin A, ya kunshi kungiyoyin kwallon kafa 4 da suka hada da Man City da PSG da RB Leipzig da kuma Club Brugge.

A rukunin B kuwa akwai Atletico Madrid da Liverpool da Porto da kuma AC Milan.

Sai rukunin C da ya kunshi Sporting da Borussia Dortmund da Ajax da kuma Besiktas.

Akwai kuma rukunin D da ya kunshiInter, Real Madrid, Shakhtar Donetsk da kuma Sheriff Tiraspol.

Sai rukunin E da ya kunshi Bayern Munich da Barcelona da Benfica da kuma Dynamo Kyiv.

Akwai kuma rukunin F da hadar da Villarreal da Manchester United da Atalanta da kuma Young Boys.

Sai rukunin G da ya kunshi Lille da Sevilla da Red Bull Salzburg da kuma Wolfsburg.

Kana rukunin H kuma na karshe da ya kunshi Chelsea, Juventus, Zenit St Petersburg da kuma Malmo.

Ga jadawalin a takaice

Group A: Man City, PSG, RB Leipzig, Club Brugge

Group B: Atletico Madrid, Liverpool, Porto, AC Milan

Group C: Sporting, Borussia Dortmund, Ajax, Besiktas

Group D: Inter, Real Madrid, Shakhtar Donetsk, Sheriff Tiraspol

Group E: Bayern Munich, Barcelona, Benfica, Dynamo Kyiv

Group F: Villarreal, Manchester United, Atalanta, Young Boys

Group G: Lille, Sevilla, Red Bull Salzburg, Wolfsburg

Group H: Chelsea, Juventus, Zenit St Petersburg, Malmo