✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Jakadan Isra’ila ya rasa gidan haya a Morocco

Da suka gano ko wane ne mai neman hayar, masu gidan babu shiri suka ki ba da hayar.

Kimanin wata shida bayan aika jakadan Isra’ila zuwa kasar Morocco, har yanzu kwana da aiki daga otel inda yake fadi tashin samun inda zai tsugunar da ofishin jakadancin.

A watan Janairu ne aka nada David Govrin a matsayin jakadan Isra’ila a kasar Morocco bayan da hukumomin Rabat suka dawo da huldar diflomasiyya da Isra’ila a bara, inda ta zama kasar Larabawa ta hudu da ta yi hakan cikin shekara biyu.

A cewar rahotannin da ke fitowa daga dukkanin kasashen biyu, masu gidajen haya a Rabat, babban birnin Morocco sun ki ba da hayar gidajensu domin tsugunar da ofishin jakadancin Isra’ilar.

“Kamfanin da aka bai wa jingar nemo matsugunin ya samo wani gidan da ya dace a wata unguwar masu hali a birnin Rabat, wanda jakada Govrin ya amince da gidan ya cika sharuddan tsaron da ake bukata,” kamar yadda wata jaridar kasar da ake wallafa wa a intanet mai suna Assahifa ta fitar a makon jiya.

“Sai dai kash! Inda matsalar take, da suka gano ko wane ne mai neman hayar, masu gidan ba tare da wata inda-inda ba sun ki ba da hayar gidansu ga jami’in diflomasiyyar Isra’ilar.”

Jaridar ta ruwaito wata majiya a kasar tana cewa irin hakan ya faru “a wasu gidajen da ke unguwar.”

Wannan lamarin ya sanya Mista Govrin, wanda tsohon jakadan Isra’ila ne a kasar Masar, har yanzu yana zama a wani otel a birnin na Rabat, a cewar jaridar.

Sanarwar dawo da huldar diflomasiyyar da kasar Morocco ta yi da Isra’ilar a watan Disamban bara ta haddasa zanga-zanga da dama a kasar domin nuna kin jinin matakin.