✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Jariri da mutum 8 sun rasu a hatsarin mota

Suna shan iska a gaban gidansu wata mota da ta kwace ta fado a kansu

Mutum tara, ciki har da wani jariri, sun riga mu gidan gaskiya bayan wata mota da ta kwace ta shiga har cikin gida ta kade su a kasar Filifins.

’Yan sanda a Arewacin kasar ta Filifins sun tabbatar cewa motar ta kwace ne a daidai wani kwana, ta auka wa wasu jerin gidaje da ke gefen wani babban titi a garin Lal-Lo da ke lardin Cagayan.

Mutanen da suka rasu, “Suna shan iska ne a gaban gidan wani abokin arzikinsu lokacin da motar da ta kwace ta fado a kansu,” a cewar Jefferson Mukay, babban jami’in dan sanda na garin Lal-Lo.

Da yake bayani a safiyar Litinin, Mukay ya bayyana cewa motar ta kwace wa matukinta ne a ranar Asabar da dare a sakamakon gudun wuce kima da yake shararawa.

Ya kara da cewa an kai direban motar da abokinsa da ke cikin motar asibiti a cikin halin rai-kwakwai-mutu-kwakwai.

Mukay ya kuma shaida wa kamfanin dillancin labarai na AFP cewa za a gurfanar da direban a gaban kotu kan zargin aikata kisa fiye da sau daya.

AFP ya ruwaito cewa ana yawan samun hatsarin mota a kasar ta Filifins, inda direbobi ke yawan saba dokokin tuki, gami da daukar kaya fiye da kima da kuma rashin kula da lafiyar motoci yadda ya kamata.

A cikin watan Janairun da ya gabata, wasu mutum 11 da ke kan hanyarsu ta zuwa casu sun rasu bayan motarsu ta kwace ta yi adungure da su a yankin Kudancin kasar.