✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Jihar Neja ta kori ma’aikata 80 kan almudahana

Ma'aikatansun yi kwanciyar magirbi kan miliyoyin kudaden gwamanti

Gwamnatin Jihar Neja ta sallami jami’anta guda 80 a ma’aikatu daban-daban bisa kama su da al’mudahanar miliyoyin kudi.

Shugabar Ma’aikata Jihar, Hajiya Salamatu Tani Abubakar ce ta bayyana wa ‘yan jarida haka bayan fitowa daga taron manyan makaraban gwamnatin jihar a ranar Alhamis.

Tani ta ce, ma’aikatan da aka sallama suna matakan ayyuka ne daban-daban kuma ana ci gaba da bincike don zakulo sauran bata-garin.

Shugabar Mai’katan ta ce, ma’ikatan sun amsa laifukansu a gaban kwamitin binciken albashi da gwamnan jihar, Abubakar Sani Bello ya kafa, kuma a yanzu haka Hukumar Ma’aikatan Jihar na kokarin rubuta musu takardun sallama.

“Ma’aikatun da abun ya shafa sun hada da: Hukumar Kula Asibitocin Jihar, mutum 45; Hukumar Shari’a, mutum 22; Hukumar Lafiya a Matakin farko, mutum 3; Ma’aikatar Lafiya, mutum 7; Ma’aikatar Ilimi mutum 1; Makarantar Ungozoma ta Minna da kuma Tunga Magajiya mutum 1 da 2 kowannensu”.

Tani ta kuma ce kwamitin na ci gaba da bincike kuma a yanzu ba zai iya bayyana yawan ma’aikata ko kudi da za su iya ganowa ba amma duk wanda aka kama da laifi zai fuskanci hukunci.