✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Kannywood: Lawan Ahmed zai tsaya takarar dan majalisa

Zai tsaya takarar ne a mazabar Bakori ta Jihar Katsina

Fitaccen jarumin masana’antar fina-finan Hausa ta Kannywood, Lawan Ahmed zai tsaya takarar kujerar Majalisar Dokokin Jihar Katsina domin wakiltar mazabar Bakori.

Jarumin wanda shi ne furodusan shirin ‘Izzar So’ mai dogon zango ya bayyana shirinsa na tsayawa takarar a shafuka sada zumuntarsa, inda yakan sanya fastar takararsa tare da rakiyar rubutun cewa, “A wajen Allah muke nema.”

A wani rubutun da ya yi na neman takarar, jarumin ya ce, “duk wadanda na lissafa za su iya fitowa takara kowace iri ce, tun daga matakin Shugaban Kasa har zuwa kansila saboda haka mu dai
a wajen Allah muke nema kuma muna neman addu’arku. Na gode,” inji shi, bayan ya lissafa wasu sana’o’i ciki har da fim da a cewarsa dukansu ’yan kasa ne kamar kowa.