✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Kano Pillars na makokin dan wasanta Bello Kofar-Mata

Marigayin dai ya rasu ya bar mata daya da ‘ya’ya.

Kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars ta aike da sakon ta’aziyar rasuwar fitaccen dan wasan kungiyar da kuma El-Kanemi Warriors, Musa Bello Kofar-Mata a ranar Talata.

Cikin sanarwa daban-daban da Kano Pillars hadi da El-Kanemi Warriors suka fitar ne suka bayyana kaduwarsu da rasuwar tare da addu’ar Allah ya jikan sa, ya kuma bai wa iyalansa hakurin jure rashinsa.

Wani makusancin margayin dai ya bayyana wa Aminiya cewa tuni an binne shi a safiyar ranar Laraba, bayan rasuwarsa cikin dare a sakamakon wata ’yar takaitacciyar jinya.

Bello Kofar-Mata ya fara kwallon kafa ne a kungiyar kwallon kafa ta Buffalos FC kafin komawa Kano Pillars, inda ya samu nasarar lashe kofin Firimiyar Najeriya (NPFL) a shekarun 2007 da 2008.

Dan wasan da ya fi kowa zura kwallo a raga a gasar NPFL din ya wakilci Najeriya a Gasar Kofin Duniya na ‘yan kasa da shekaru 20 da aka yi a Canada a shekarar 2007.

Marigayin ya fara buga wa babbar kungiyar a shekarar 2010, a wasan da suka lashe da ci 5-2 da Jamhuriyar Dimokuradiyyar Kongo.

Ana iya tunawa cewa, a shekarar 2007 ne Kofa-Mata ya rattaba hannu kan wata yarjejeniya da kungiyar kwallon kafa ta IK Start ta kasar Norway, kafin zuwansa LASK ta Australiya a 2008 a matsayin dan wasan aro.

Marigayin dai ya rasu ya bar mata daya da ‘ya’ya.