✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Kano Pillars ta koma saman teburin Firimiyar Najeriya

A yanzu Pillars ta hada maki 48 kenan cikin wasanni 25.

Kungiyar Kano Pillars ta haye saman teburin gasar Firimiyar Najeriya bayan ta lallasa Enyimba International da ci 2-1 a wasan mako na 25 da suka fafata ranar Lahadi.

Yayin haduwar tasu, Enyimba ce ta fara zura kwallo a ragar Pillars ta hannun Victor Mbaoma kuma haka sakamakon ya kasance har aka tafi hutun rabin lokaci.

Bayan dawowa ne Kyaftin din Pillars, Rabi’u Ali ya farke mata a bugun daga kai sai mai tsaron raga.

Yayin da ya bai wuci saura minti 15 a tashi daga wasan ba, Pillars ta kara kwallo ta biyu ta hannun Ifeanyi Eze da hakan ya bai wa kungiyar maki ukun da take bukata.

Da wannan sakamako ne Pillars wacce take bani in baka wajen jan ragamar teburin Firimiya Najeriya a bana da Akwa United, yanzu ta koma ta daya a makon nan.

A yanzu Pillars ta hada maki 48 kenan cikin wasanni 25, yayin da ita kuwa Akwa United ta samu maki daya bayan ta tashi 2-2 a gidan Wikki ranar Lahadi.

Ga yadda sakamakon mako na 25 da aka buga ranar Lahadi a gasar Firimiyar Najeriya ya kasance:

Abia Warriors 1-1 FC IfeanyiUbah

Adamawa United 0-2 Plateau United

Dakkada FC 0-1 Lobi Stars

Heartland FC 2-2 Rivers United

Kano Pillars 2-1 Enyimba International

Rangers International 1-1 MFM FC

Katsina United 2-1 Nasarawa United

Kwara United 3-0 Jigawa Golden Stars

Warri Wolves 2-1 Sunshine Stars

Wikki Tourists 2-2 Akwa United