Dubban ma’aikata ne suka tsunduma yajin aiki a fadin Afirka ta Kudu a kokarin ganin an yi masu karin albashi da kuma inganta walwalar yanayin aiki.
Kafafen yadda labaru na cikin gida na cewa wannan ne karo na farko da ma’aikatan gwamnati na kasar suka shiga irin wannan yajin aikin a cikin shekara goma.
- Budurwa ta jefa kanta cikin teku a Legas
- ‘Na shafe watanni 6 ina sayar da zobon da na hada da jinin cutar kanjamau’
Ana sa ran yajin aikin zai kawo cikas ga tafiyar da lamurra a ma’aikatun gwamnati da filayen jirgin sama.
Fara yajin aikin ya biyo bayan kasa cimma matsaya tsakanin Kungiyar Kwadago ta kasar da bangaren gwamnati.
Kungiyar na bukatar a yi wa ma’aikata karin albashi na kashi 7%, yayin da gwamnati ta dage a kan karin kashi 3%.