✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Karin kasafin N894bn: Buhari ya nemi yardar Majalisar Wakilai

Shugaban Kasar ya ce kasafin na sayen makamai ne da kuma allurar rigakafin COVID-19.

Shugaba Buhari ya aike wa Majalisar Wakiali takardar bukatar amincewarta da karin kasafin N894bn domin sayen makamai da allurar rigakafin COVID-19.

Takardar neman amincewar da Shugaban Majalisar, Femi Gbajabiamila, ya karanta a ranar Talata ta ce karin kasafin ya mayar da hankali ne kan wasu muhimman bukatu.

Sauran bukatun kuma za a sanya su a cikin kasafin shekarar 2022, wadda ake sa ran gabatarwa a watan Satumba, 2021.

Ta ce karamin kasafin zai tabbatar da samar da makamai da sojoji za su yi amfani da su wajen samar da tsaro.

Ragowar kuma za a yi amfani da su domin tabbattar da ganain an yi wa kashi 70% na ’yan Najeriya da suka cancanta allurar rigakafin COVID-19, daga yanzu zuwa shekarar 2022.