✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Kasar Kamaru ta fara gasar AFCON 2021 da kafar dama

A halin yanzu Burkina Faso ce a kasan teburin rukunin A.

Tawagar kasar Kamaru da ake yi wa lakabi da The Indomitable Lions, ta fara da kafar dama a wasanta na farko wanda ta bude gasar Kofin Nahiyyar Afirka na AFCON 2021, inda ta yi nasara da ci 2-1.

Kamaru ta shige gaban Burkina Faso a zagayen farko na wasansu a gasar da suke bude a yau Lahadi, 9 ga watan Janairun 2022.

Bayanai sun ce shugaban kasar Kamaru, Paul Biya da Samuel Etoo, sabon shugaban Hukumar Kwallon Kafar Kamaru suna cikin wadanda suka kalli wasan da aka fafata a filin wasanni na Paul Biya da ke Olembe a Yaounde, babban birnin kasar.

A dai-dai minti na 25 ne dan wasan tsakiyar Burkina Faso, Gustavo Sangare na Kungiyar Al-Nassr ya jefa kwallon farkon a raga bayan kwarbar da aka sha a yadi na goma sha takwas na bangaren gidan Kamaru.

Mintuna 3 kafin tafiya hutun rabin lokaci ne Kamaru ta samu bugun daga kai sai mai tsaron raga, inda a nan dan wasan tsakiyarta Aboubakar wanda shi ke mata goma da kaftin ya zare kwallon.

Daf da za a tafi hutun rabin lokacin ne dan wasan baya na Burkina Faso, Nouhou Tolo ya yi wa Issoufou Dayo na Kamaru keta a raga, lamarin da ya sa alkalin wasa ya sake ba su bugun daga kai sai mai tsaron raga, kuma Aboubakar bai yi wata- wata ba ya sanya kasarsa Kamaru a gaba.

A haka aka nade tabarmar nishadin da sakamakon wasan a 2-1, lamarin da ya bai wa Kamaru damar darewa teburin rukunin A na gasar.

A halin yanzu Burkina Faso ce a kasan teburin rukunin A, inda kasashen biyu za su buga wasansu na gaba a ranar 13 ga watan Janairu.

A wasanninsu na gaba, Kamaru wadda ita ce mai masaukin baki a gasar za ta fafata da Ethiopia (Habasha), yayin da ita kuma Burkina Faso za ta barje gumi da Cape Verde.