✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Kotu ta daure tsohon jami’in Kwastam kan fasakwaurin bindigogi

Kotun ta kuma ba da umarnin a damka bindigogin ga Gwamnatin Tarayya.

Babbar Kotun Tarayya da ke Legas ta yanke wa wani tsohon jami’in Hukumar Kwastam ta Najeriya tare da wasu mutum biyu hukuncin daurin shekara 16, bisa laifin shigo da bindigogi 661 ba bisa ka’ida ba.

Kotun, wadda ke karkashin Mai Shari’a Ayokunle Fajji, ta sami Mahmud Hassan da kamfaninsa, da Oscar Okafor da kuma Donatus Achinulo, da laifin hada baki wajen yin fasakwaurin bindigogin.

Sai dai kotun ta wanke, ta kuma sallami daya daga cikin wadanda aka tuhuma, Abdullahi Danjuma. daga dukkan zarge-zargen.

A cikin kunshin tuhume-tuhumen da ake musu dai, Babban Lauyan Gwamnati, kuma Ministan Shari’a, Abubakar Malami, ya zarge su da shigo da makaman daga kasar Turkiyya ta tashar jiragen ruwa ta Apapa da ke Legas.

Ya ce an shigo da bindigogin ne a cikin wata kwantena mai zurfin kafa 40, wadda aka yi karyar cewa kamaren karfe ne a cikinta.

Takardun bogi

Kazalika, an samu wadanda ake zargin da yin takardun kwantenar na bogi don yin fasakwaurin cikin sauki.

Daga nan sai Kotun ta yi umarnin a damka bindigogin ga Gwamnatin Tarayya.

Kazalika, ta umarci a rufe kamfanin da aka yi amfani da shi wajen fasakwaurin, yayin da ta umarci a ba Gwamnatin Tarayya dukkan kadarorinsa.

Da yake yanke hukunci, Alkalin ya ce laifin da mutanen suka aikata mai girma ne saboda ya shafi tsaron kasa.