✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Kotu ta hana magoya bayan Peter Obi yin gangami a Legas

Kotun ta hana su gangamin ne a tol get din Lekki

Babbar Kotun Jihar Legas ta bai wa jm’iyyar LP da magoya bayanta umarnin kada su kuskura su gudanar da gangamin siyasa a ‘tol get’ din Lekki da ke jihar.

Kotun, wacce ke karkashin Mai Shari’a Daniel Osiagor, ta hana gangamin ne mai taken #ObiDatti23 Forward Ever Rally’ wanda magoya bayan dan takarar jam’iyyar, Peter Obi suka shirya gudanarwar ranar daya ga Oktoba, 2022.

Sai dai kotun ta ce ba ta hana magoya bayan gudanar da gangaminsu a sauran wurare hudun da suka shirya yin hakan a jihar ba.

Duk da umarnin hanin, kotun ta ce babu laifi masu gangamin na iya shigewa ta tol get su wuce zuwa sauran wurare, amma babu tsayawa ko hada taro a wajen.

Tol get din na Lekki dai na dada samun tagomashi ne tun bayan hargitsin da ya auku lokacin zanga-zangar #EndSARS a watan Oktoban 2020.

Lamarin da ya kai ga asarar rayuka wanda ya yi sanadiyar rufe kofar na wani lokaci.