✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Kotu ta raba auren shekaru 15 saboda cin amana

Kotun ta amince da raba auren saboda samun masalaha a tsakanin ma'auratan.

Wata kotu dake zamanta a Ile-Tuntun a Ibadan ta raba auren shekara 15 tsakanin Adeyemi Bamigbola da Bidemi, kan zargin cin amana.

Mai shari’a Cif Henry Agbaje ne ya yanke hukuncin a ranar Laraba, don kawo karshen tashin-tashina a tsakanin ma’auratan.

Bayan raba auren, alkalin kotun ya umarci Bamigbola da yake bai wa matar dubu goma duk wata domin kula da yaransa guda biyu.

Tun farko Bamigbola ne ya shigar da kara gaban kotun, inda ya bukaci ta raba aurensa da matarsa, saboda neman maza da take yi.

Ya ce “Jami’an ‘yan sanda a Oyo sun taba kama mata da wani saurayinta mai suna Jomo suna aikata fasikanci.”

Da take maida martani, Bidemi, wacce ‘yar kasuwar ce, ta ce “Bamigbola ba mutum kirki ba ne don ko daukar dawainiya ta da yaranmu ba ya yi.”

“Akwai lokacin da aka taba yunkurin korarmu daga gidan haya, saboda ya gaza biya sai bashi na karbo na biya kudin hayar.”

Kazalika, ta koka kan yadda mijin nata yake shan giya da bin matan banza.

Ta ce, “na sha kama shi da matan banza a kan gadonmu na aure.”

Saboda wannan tirka-tirka da aka dinga fama da ita kotun, ta yanke hukuncin raba auren don samun masalaha.