✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Kotu ta wanke Aminu Wali daga zargin miliyan N950

EFCC ta na duba yiwuwar daukar wani mataki bayan kotu ta yi watsi da karar

Babbar Kotun Tarayya da ke Kano ta wanke Tsohon Ministan Harkokin Wajen Najeriya, Ambasada Aminu Bashir Wali daga zargin karkatar da Naira miliyan 950.

Kotun ta wanke Ambasada Wali ne tare da tsohon Kwamishinan Ayyuka na Jihar Kano, Mansur Ahmad da ake tuhumar su da kwanciyar magirbi da kudaden yakin neman zaben 2011.

Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa (EFCC) ce ta gurfanar da su bisa zargin karbar kudaden ba tare da bin ta banki ba, sabanin dokar safarar da haramtattun kudade ta 2011.

Da yake yanke hukunci, alkalin kotun, Mai Shari’a Lewis Allagoa ya ce bangaren masu gabatar da kara sun kasa tabbatar da zargin da suke yi.

Don haka ya yi fatali da karar hukumar ya kuma wanke wadandada ake zargin.

Ambasada Wali ta bakin lauyansa, Sam Olagunorisa ya ce sun ji dadin wankewar da kotun ta yi musu, ya kuma kara da cewa kudaden da ake zargi sun bi da hannun halastacciyar cibiyar kudi.

Lauyan EFCC, Cosmos Ogwu, a nasa bangaren, ya ce maganar ta kare, tun da dama shari’a sabanin hankali ce.

Sai dai ya ce: “Za mu kara nazarin hukuncin mu ga abin da za mu iya yi daga baya”.