✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

‘Ku Ilmantar Da Mata Muhimmancin zaben ’Yan Takara Nagari’

Majalisar Kungiyoyin Mata ta Najeriya (NCWS) ta ce wayar da kan mata kan zaben ’yan takarar da suka cancanta a zaben 2023 na da matukar…

Majalisar Kungiyoyin Mata ta Najeriya (NCWS) ta ce wayar da kan mata kan zaben ’yan takarar da suka cancanta a zaben 2023 na da matukar muhimmaci.

Shugabar kungiyar, Priscila Kuye, ta bayyana wa taron shekara da suka shirya kan muhimmacin sanya mata a sha’anin gwamnati a ranar Alhamis cewa yin hakan ya zamo dole, saboda yawan matan da ke fita yin zabe a Najeriya ya fi na maza.

“Kada ku bar wa maza komai, domin idan ana batun sha’anin mata ba su san inda ke mana kaikayi ba.

“Ku karfafa wa kanku da ’ya’yanku mata guiwar shiga harkokin siyasa, da kuma zabar mutanen da suka cancanta a 2023, domin ba kansu kadai za su zabowa ba, har da ku ma,” in ji ta.

Ta kuma yi kira ga al’umma da su kara ba wa mata gudummawar da ta dace, domin hakan ba iya rayuwarsu zai inganat ba, har ma da tattalin arziki, da zamantakewa da siyasar Najeriya.