✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Ku zo mu hada kai don ciyar da Gombe gaba – Gwamna ga ’yan adawa

Ya bayyana hake ne lokacin da ya karbi shaidar kashe zabe

Gwamna Muhammad Inuwa Yahaya na Jihar Gombe, ya yi kira ga ’yan jam’iyyar adawa da su zo a hada kai da gwamnatinsa don kara dora jihar a turbar ci gaba.

Gwamnan ya yi wannan kiran ne a ranar Alhamis, jim kadan bayan Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta mika masa takardar shaidar cin zabe, karo na biyu.

An ba shi shaidar ce tare da Mataimakinsa, Manasseh Daniel Jatau da ’ƴan majalisan dokokin jihar a ranar 18 ga watan Maris.

“Ina kira ga duk wadanda suka tsaya takara a zaben da ya gabata da su zo mu hada kai wajen ba da shawarwari na gari don ciyar da jihar mu gaba,” in ji Gwamnan.

Ya kuma kara tabbatar wa al’ummar Jihar Gombe cewa takardar shaida da ya karba shaida ce ta nuna cewa zai kara kwazo da himma dan karasa ayyukan da ya faro da kuma aza tubalin wasu sababbi.

Ya yaba wa hukumar INEC kan yadda ta bullo da sabbin dabaru a kokarinta na inganta harkokin zabe a Najeriya.

A jawabinsa na maraba, Kwamishinan hukumar zaben a Jihar Gombe Alhaji Umar Ibrahim, ya bukaci wadanda suka yi nasarar da su dauki nasarar tasu a matsayin amanar da masu zabe suka dora musu don ganin jihar da al’umma sun shaida ribar mulkin Dimokuradiyya.