✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Kungiyar Tarayyar Afirka ta zabi sabon shugaba

Shugabannin sun yi kakkausar suka kan jerin juyin mulkin da aka yi a baya-bayan nan.

A yayin taron kolinta karo na 35 da ta gudanar a karshen mako, kungiyar Tarayyar Afirka wato AU, ta zabi Shugaban kasar Senegal wanda zai jagorance ta na wani sabon wa’adi.

Kungiyar Tarayyar Afirka ta zabi shugaban kasar Senegal Macky Sall, a matsayin sabon shugabanta na wa’adin shekara guda.

Kungiyar ta zabi shugaban na Senegal ne yayin taron da ta gudanar a shelkwatarta da ke Addis Ababa, babban birnin kasar Habasha, bayan karewar wa’adin Felix Tshisekedi na Jamhuriyar Dimukuradiyyar Congo.

A karshen taron koli da suka kammala a ranar Lahadi, shugabannin sun yi kakkausar suka kan jerin juyin mulkin da aka yi a baya-bayan nan a wasu kasashen nahiyar wanda ya janyo kungiyar ta dakatar da kasashen daga wakilci a cikinta.

Shugabannin sun kuma dakatar da muhawara a game da wakilcin kasar Isra’ila a matsayin ’yar kallo a kungiyar, wanda shugaban hukumar gudanarwarta Moussa Faki Mahamat, ya amince da batun cikin watan Yulin bara.