✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Kwanan nan za a fara kashe kudaden Najeriya a China

Bankunan Najeriya da China za su fara aiki a kasashen biyu.

Bankunan kasar China za su fara karbar kudaden Najeriya nan gaba, kuma bankunan China za su shigo Najeriya domin fara aiki.

Jakandan kasar China a Najeriya, Cui Jianchun, ya sanar da cewa hakan zai taimaka wajen bunkasawa tare da saukaka gudanar da harkokin kasuwanci da zuba jari a tsakanin kasashen biyu.

Ya ce ofishinsa na aiki ka’in da na’in domin tabbatar da ganin bankunan Najeriya sun fara aiki a kasashen biyu, kuma “Manyan bankunan kasashen biyu na kokarin fara aiwatar da yarjejeniyar amfani da kudadensu a tsakaninsu; kuma za a fadada tsarin.

“Yanzu haka ina aiki domin ganin bankunan kasar sun shigo Najeriya sun fara aiki, bankunan Najeriya ma suna aiki a China,” inji shi.

Da yake bayani a wata tattaunawa da manema labaria a Abuja, hakan zai saukaka amfani da kudaden China da Najeriya a tsakaninsu wajen gudanar da kasuwanci da harkar masana’antu.

Mista Jianchun, ya yi fatan samun fahimtar juna tsakananin majalisun dokokin kasashen biyu a kan hakan.

Ya ce a watan Nuwamba mai kamawa ne za a gudanar ta taron ministocin kungiyar hadin kan kasashen Afirka da China karo na takwas a kasar Senegal.