✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Ma’aikatan shari’a za su tsunduma yajin aiki

Kungiyar ta umarci dukkanin mambobinta da su kulle ma'aikatu da kotuna a fadin Najeriya.

Kungiyar Ma’aikatan Shari’a ta Kasa (JUSUN), reshen Jihar Kano, ta shirya shiga yajin aiki daga ranar 6 ga Afrilun 2021.

Hakan na dauke ne a sanarwa da Shugaban JUSUN, reshen Jihar Kano, Mukhtar Rabiu Lawan ya fitar a ranar Litinin.

“Wannan mataki ya biyo bayan umarnin da uwar kungiya ta kasa ta bayar. Don haka za mu tafi yajin aiki tare da kulle dukkanin ma’aikatun shari’a da kuma kotuna,” a cewar Lawan.

Kazalika, shugaban ya ce reshen Kano na JUSUN na umartar dukkan mambobinta da su rufe kotuna da ma’aikatun shari’a na jihar har sai an samu karin bayani daga uwar kungiyar ta kasa.

Tun a ranar 1 ga watan Afrilyu, uwar kungiyar JUSUN ta kasa ta ba da umarnin shiga yayin aikin.