✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Magidanci ya kashe matarsa da dansa

Mutum ya yi wa iyalan nasa mummunan kisa

Wani magidanci mai ya kashe matarsa da dansa mai shekara hudu ta hanyar amfani da shebur.

Majiyar Aminiya ta ce magidancin ya hallaka matarsa da dan nasa ne ta hanyar bubbuga musu shebur din da ya yi amfani da shi a kai.

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, kakakin ’yan sandan jihar Anmabra, CSP Haruna Mohammed, ya ce “mutumin ya farmaki matarsa da dansa mai shekara hudu, ya buga musu shebur a kai.”

Mutumin ya kuma yi amfani da shebur din wajen kai farmaki wa wani dan banga kafin daga baya a kama shi.

CSP Haruna ya ce bayan samun rahoton faruwar lamarin, ‘yan sanda sun garzaya da matar da yaron zuwa asibitin Ozubulu, ina likita ya sanar da cewa sun mutu.

Jami’in ya kuma bayyana cewa dan bangar da mutumin ya farmaka da shebur na murmurewa a asibiti.

Ya ce abin alhinin ya faru ne a kauyen Ofufe Nza a Karamar Hukumar Ekwusigo, da ke Jihar ta Anambra, inda jami’an Rundunar suka cafke wanda ake zargin a ranar Talata da misalin karfe 7:45.

Sai dai kuma ya kara da cewa ana zargin cewa magidancin da ya yi danyen aikin na fama da tabin hankali.

Kwamishinan ’yan sandan jihar, CP John Abang, ya ba da umarnin a ci gaba da binciken wanda ake zargin a sashen binciken manyan laifuka na Rundunar domin gano abin da ya faru.