✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Mai Garin Lakwaja ya rasu yana da shekara 80

Alhaji Muhammad Kabir Maikarfi III ya rasu bayan shekara 30 a kan karagar mulki

Allah Ya yi wa Mai Garin Lakwaja, Alhaji Muhammad Kabir Maikarfi III, rasuwa yana da shekara 80 a duniya.

Masarautar Lakwaja, ta sanar da rasuwar Babban basaraken, wanda shi ne Shugaban Majalisar Masarautar ta ce ya rsu ne bayan rashin lafiya a wani asibiti mai zaman kansa a Abuja.

Sanarwar da Sakataren Masarautar Lakwaja, Muhammed Nalado Usman, ya fitar a ranar Laraba da dare ta ce za a yi jana’izar basaraken ne da misalin karfe 4 ranar ALhamis a garin Lakwaja.

Alhaji Muhammad Kabir Maikarfi III ya rasu ne bayan shekara 30 a kan sarautar Mai Garin Lakwaja, wanda ya samu tun a shekarar 1992.