✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Malama ta gurfanar da mijinta saboda rashin cin abinci

Ya sa ’ya’yan da muka haifa sun dora mata karan-tsana.

Wata malamar makaranta mai suna Joy Eze, ta yi karar mijinta Nuel Chukwu a gaban wata Kotun Al’adu saboda kaurace wa abincinta.

Jaridar Daily Nigerian ta ruwaito cewa, matar ta yi karar mijin ne kan zarginta da yake yi na zuba masa guba a abinci.

Da take gabatar da bukatar neman a tsinka igiyar aurensu a gaban kotun mai zamanta a Unguwar Jikwoyi da ke Abuja, Joy ta ce ba za ta iya ci gaba da zama da shi ba.

Joy wadda ta nemi a raba auren, ta kuma rokin kotun ta ba ta rikon ’ya’yansu.

“Ya daina cin abincina, idan kuma na nemi jin bahasi sai ya ce yana sane da kulle-kullen da nake yi don ganin bayansa.

“Ya riga ya sanar da ’yan uwansa cewa a duk lokacin da ya mutu to alhakin yana wuyana, a cewarta.

Joy ta kuma shaida wa kotun cewa, mijin nata ya sa ’ya’yan da suka haifa sun dora mata karan-tsana.

“Ya bata min suna a wurin yayana saboda irin munanan abubuwan da yake fada musu a kaina.

“Ya sanar da su [’ya’yana] cewa karuwanci nake fita kuma duk kayayyakina da takalma da jakunkuna ’yan dadiro ne suka saya min.”

A nasa martanin, mijin Joy wanda ke sanaar kabu-kabu da babur mai kafa uku, ya musanta zarge-zargen da matar ke yi masa.

Alkalin kotun, Labaran Gusau ya dage sauraron karar zuwa ranar 21 ga watan Satumba.