✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Mamakon ruwan sama ya hana kammala bikin gasar ninkaya a Legas

Za a sanar da ranar kammala gasar a nan gaba

Wani ruwan sama da aka tafka kamar da bakin kwarya ya hana kammala bukukuwan gasar ninkaya da bankin Zenith ga shirya wa makarantun firamare a Jihar Legas.

Gasar dai, wacce daya ce daga cikin hanyoyin bunkasa ninkaya a Najeriya na dab da farawa ne a filin Ikoyi Club kafin ruwan ya fara sauka.

A cewar Shugaban shirya ninkayar, Kunle Adeniji, “Tilas ta sa muka dauki wannan matakin ba don muna so ba, sai don kiyaye lafiyar masu fafatawa a cikinta da kuma tabbatar da yin adalci.”

Ya ce nan ba da jimawa ba za a sanar da ranar da za a kammala gasar.

Shi ma Shugaban Kungiyar Masu Wasanni a Ruwa ta Najeriya, Babatunde Fatayi-Wiliams ya ce an dauki matakin ne bisa la’akari da dokokin kasa da kasa.

Jimillar makarantun firamare 14 ne suke fafatawa a gasar da masu ninkaya 226.

Adeniji ya kuma yaba wa bankin tare da dukkan masu shirya gasar da makarantun da suka fafata a ciki saboda hadin kan da suka bayar har ta samu nasara.