✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Masarautar Saudiyya ta yi bikin wanke Ka’abah

Wanke dakin Ka’abah ya faro ne tun daga lokacin Annabi Muhammad (SAW).

Masarautar Saudiyya mai kula da Masallatan Harami ta yi bikin wanke Ka’abah da aka saba duk shekara bayan kammala aikin Hajji.

A madadin Sarki Salman bin Abdul Aziz al Saud, Yarima mai jiran gado, Muhammad bin Salman tare da Shugaban Masallatan Harami, Sheikh Abdul Rahman al-Sudays da kuma Limaman Masallatan Haramin ne suka jagorancin wankin Dakin Allah.

Shafin intanet na Haramain, wanda ya wallafa hotunan wankin Ka’abah, ya ce an gudanar da shi ne a safiyar Talatar nan.

Ana amfani ruwan zam-zam da turaruka masu kamshi, ciki har da miski da kuma tawul mai tsabta wajen wanke dakin Ka’abah.

Akan tanadi dukkan abubuwan da ake bukata kwana guda kafin a wanke dakin.

BBC ya ruwaito cewa, ana shafe sa’o’i biyu wajen wanke dakin.

Wanke dakin Ka’abah ya faro ne tun daga lokacin Annabi Muhammad (SAW).