✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Masu garkuwa da mutane 13 sun shiga hannu a Adamawa

’Yan sanda sun kama wasu mtum 13 da ke garkuwa da mutane domin karbar kudin fansa a Jihar Adamawa.

’Yan sanda sun kama wasu mtum 13 da ke garkuwa da mutane domin karbar kudin fansa a Jihar Adamawa.

Dubun masu garkuwa da mutanen ta cika ne bayan ’yan sanda sai kai samame a maboyar bata-garin inda suka kwato bindigogi biyar da sarkar daure mutanen da suka sace.

Da yake gabatar da bata-garin, Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Adamawa, SK Akande, ya kara da cewa an kwace kayan sojoji da tsabar kudi N358,500 daga hannunsu.

Kwamishinan ’yan sandan ya ce an yi wa masu garkuwa a mutanen dirar mikiya a maboyarsu ne bayan samun bayanan sirri.

Ya kara da cewa rundunar ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen farauta da kuma kamo sauran bata-garin da suka tsere.