✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Matar Sheikh Zakzaky ta kamu da Coronavirus

Gwaji da likitoci suka gudanar ya tabbatar Zeenatu tana dauke da kwayar cutar Coronavirus.

Matar Sheikh Ibrahim El-Zakzaky, Shugaban Kungiyar IMN wadda aka fi sani da Shi’a a Najeriya, Zeenat El-Zakzaky, ta kamu da cutar Coronavirus.

Mai magana da yawun kungiyar, Ibrahim Musa ne ya inganta rahoton a wata zantawa da ya yi da BBC Hausa.

’Yan bindiga sun sace mutane da dama a kauyen Zamfara

Sarkin Anka ya mayar da martani kan zarginsa da dakile shirin zaman lafiya

Kazalika, cikin wani rahoton da dan malamin, Sayyid Ibahim Zakzaky ya wallafa a shafinsa na Twitter ranar Alhamis, ya ce mahaifiyarsa ta kamu da cutar Coronavirus bayan likitoci sun gudanar da gwaje-gwaje domin duba lafiyarta.

Ya wallafa cewa, kwanaki shida da suka gabata bayan likitocin da ke duba lafiyar mahaifana sun ziyarce su a gidan yarin Kaduna, mahaifiyata ta yi korafin tana jin kasala da zazzabi kuma ba ta iya tantance kamshi ko wari.”

Ya ce dalilin haka ya sanya aka yi mata gwaje-gwaji cikin har na da na coronavirus inda aka tabbatar tana dauke da kwayar cutar.

Ya zuwa yanzu dai gwamnatin Jihar Kaduna ba ta ce uffan a kan wannan lamari ba ballantana na bullar cutar a gidan yarin jihar.

Tun a watan Dasumba na shekarar 2015 Sheikh Zakzaky da matarsa Zeenatu ke tsare bayan wata mummunar arangama da mabiyansa suka da wata tawaga ta Rundunar Sojin Kasa a garin Zaria.