✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Matsalar tsaro: An sake tsawaita hutun makarantun Kaduna

Gwamnatin dai ta ce za a sanar da sabuwar rana da zarar tsaro ya inganta.

Gwamnatin Jihar Kaduna ta sanar da tsawaita lokacin sake bude makarantu a Jihar saboda kalubalen tsaro.

A baya dai, Jihar ta sanar da ranar tara ga watan Agustan 2021 a matsayin ranar da za a sake bude makarantu don fara sabon zangon karatu na uku.

Sai dai gwamnatin ta ce ayyukan da dakarun soji ke gudanarwa yanzu haka ta sama da kasa kan ’yan bindiga a iyakarta da Jihohin Neja da Katsina da Filato da kuma Zamfara ba za su bari a sake bude makarantun ba.

Kwamishinan Ilimi na Jihar, Shehu Usman Muhammad, da takwaransa na Tsaro da Al’amuran Cikin Gida, Samuel Aruwan, ne suka bayyana hakan a cikin wata sanarwar hadin gwiwa ranar Juma’a.

Sun ce Jihar ta kuma umarci jami’an tsaro da su dada zafafa kai hare-hare a sabbin maboyar ’yan bindigar da aka gano a kwanan nan.

“Gwamnatin Jihar Kaduna ta karbi shawarwarin tsaron da aka bata, kuma a kan haka take umartar dukkan makarantu da su bi wannan umarnin sau da kafa.

“Za a sanar da sabuwar ranar sake bude makarantun da zarar al’amuran tsaro sun inganta,” inji sanarwar.