✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Mazauna Saudiyya 60,000 ne kadai za su yi aikin Hajjin bana

Tun bayan bullar cutar COVID-19 ake samun ragin adadin mutanen da za su aikin hajji.

Masarautar Kasar Saudiyya ta sanar da cewar iya mutum 60,000 ’yan asalin kasar da wanda suke zaune a cikin kasar ne kadai za su yi aikin Hajjin bana.

Shafin Haramai Sharifain da ya sanar da hakan ya ce wannan na zuwa ne a matsayin wani mataki na ci gaba da yaki da kuma dakile cutar COVID-19 a fadin duniya.

  1. An rufe Kwalejin Nuhu Bamalli da ke Zariya
  2. Ganduje ya sha alwashin hukunta masu daukar nauyin fadan daba a Kano

Mutum 60,000 da ke zaune a kasar, ciki har da wadanda ba ’yan asalin kasar ba na da damar yin aikin hajjin a bana, kamar yadda sanarwa ta gabatar a ranar Asabar.

Kazalika, Hukumar Lafiyar Kasar ta bayyana cewar tilas ne, ga wanda zai yi aikin hajjin a bana, ya kasance ya karbi akalla rigakafin allurar COVID-19 kashin farko, tare da killace kansa na tsawon mako biyu.

Tun a cikin watan azumi, kasar ta sanar da adadin mutum 60,000 a matsayin wanda za su aikin hajjin bana, amma ba ta ba da cikakken bayanin wanda zai halarta ba sai a yanzu.

A shekarar da ta gabata ma mutum 10,000 ne kacal suka gudanar da aikin Hajjin sakamakon bullar cutar COVID-19.

Sai dai a wannan shekarar, an samu karin adadin mahajjata da za su yi aikin hajjin fiye da na bara.