✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Motar dakon mai ta turmushe mutum 5 a Ibadan

Hatsarin ya auku yayin da motar da kwace kuma ta yi kan ’yan kasuwa.

Kimanin mutum biyar ne suka yi gamo da ajalinsu yayin da wata babbar motar dakon iskar gas ta turmushe su a ranar Lahadi.

Aminiya ta ruwaito cewa, mutanen da karar kwana ta cimma na daga cikin wadanda motar ta afka kansu a Kasuwar Bode da ke Ibadan, babban birnin Jihar Oyo.

Kakakin rundunar ’yan sandan jihar, Adewale Osifeso ya tabbatar da faruwar lamarin.

A cewarsa, hatsarin ya auku ne yayin da motar da kwace wa direban a yankin Idi-Arere kuma ta yi kan ’yan kasuwar.

Sai dai binciken da wakilinmu ya gudanar ya gano cewa mutanen da suka riga mu gidan gaskiya sakamakon hatsarin sun kai goma.

A cewar Mista Osifeso, mutane da dama sun jikkata kuma jami’ansu na ci gaba da fadada bincike domin fidda cikakken bayani a kan lamarin.

Hadin gwiwar jami’an hukumar kashe gobara da ’yan sanda sun taru a wurin yayin da lamarin ya auku da zummar dakile duk wani abu da ka iya zuwa ya dawo.