✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Mun bankado sunan jariran da ake biya albashi daga lalitar Borno – Zulum

Ya ce an gano hakan ne bayan aikin tantance ma’aikatan da aka yi.

Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya ce an bankado sunan jarirai a jerin wadanda ake biya albashi daga lalitar Jihar.

Ya ce an gano sunayen ne a Karamar Hukumar Shani ta Jihar, bayan aikin tantance ma’aikata a Jihar.

Ana dai zargin cewa wasu jami’an gwamnati ne ke wawure albashin ma’aikatan bogin da ake da su a fadin Jihar.

Ya bayyana hakan ne yayin bikin al’adu na Menwara a garin Shani, ranar Asabar.

Gwamna Zulum ya ce tun da farko an kirkiro shirin tantance ma’aikatan ne domin gano na bogi daga cikinsu, amma masu adawa da hakan a Karamar Hukumar suka shirya zanga-zangar rashin nuna goyon baya.

Ya ce, “Ina sanar da ku cewa bayan kammala tantancewar, mun bankado sunayen jarirai a jerin ma’aikata, yayin da muka kuma gano cewa a duk wata, akan kashe Naira miliyan 19 wajen biyan ma’aikatan bogi a kowanne wata a Karamar Hukumar Shani.

“Akwai iyali daya da muka gano sunan ma’aikatan bogi 300. Ina fargabar in hakan ya ci gaba, akwai yiwuwar Karamar Hukumar ta gaza biyan albashi a nan gaba kadan,” inji Gwamnan.

Ya kuma yi zargin cewa guraben ayyukan da ya kamata a ba mutanen Karamar Hukumar ana sayar wa wasu akan N250,000, lamarin da ya ce yana hana matasan da suka yi karatu samun aiki.