✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Mutum 2 sun mutu a hatsarin babur a Akure

Mutum biyu ne suka mutu sakamakon hatsarin.

Mutum biyu sun riga mu gidan gaskiya sakamakon hatsarin da ya auku a Akure, babban birnin Jihar Ondo.

Hatsarin ya faru ne da jijjifin safiyar Laraba bayan da wani dan acaba mai dauke da fasinjoji biyu ya yi gwabza wa wata babbar mota.

Majiyarmu ta ce, dan acaba ya dauki fasinjojin ne da nufin kai su asibiti inda suka gamu da iftila’in.

Hatsarin ya faru ne a yankin Oba-Ile cikin Karamar Hukumar Akure ta Arewa a jihar.

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) ya rawaito ana zargin rashin fitula a babur din da gudun wuce kima ne dalilan da suka haifar da hatsarin.

Mai magana da yawun ‘yan sandan jihar, SP Olufunmilayo Odunlami-Omisanya, ya tabbatar da aukuwar hatsarin, inda ya ce an kwashi gawargwakin zuwa Asibitin Kwararru da ke Akure.