✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Mutum 9 sun kamu da Kyandar Biri a Abiya

Hukumar NCDC ta ce cutar kyandar biri ta kashe mutum dudu, wasu 172 kuma sun kamu da ita a Najeriya a 2022.

Gwamnatin Jihar Abiya ta tabbatar cewa mutum tara sun kamu da cutar Kyandar Biri a fadin jihar.

Babbar Jami’ar Lafiya ta jihar, Misis Peace Nwogwugwu ce ta bayyana hakan a Umuahia babban birnin jihar a ranar Laraba.

Ta ba da tabbacin ne sa’ilin da take jawabi a wajen taron kara wa juna ilimi na yini daya da Kungiyar Mata ’Yan Jarida ta Najeriya (NAWOJ) tare da hadin gwiwar Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Abiya suka shirya.

Ta ce, “A halin da ake ciki, an gudanar da bincike a kan mutum 40 da ake zargin sun kamu da Kyandar Biri, inda aka tabbatar da mutum tara daga kananan hukumomi biyar a jihar na dauke da cutar.”

Ta kara da cewa, kananan hukumomin da lamarin ya shafa sun hada da, “Umuahia ta Arewa da Umuahia ta Kudu da Ikwuano da kuma Umunneochi wadanda kowacce ke da mutum biyu-biyu da suka kamu da cutar, sai kuma karamar hukumar Aba ta Arewa da ke da mutum daya.”

“Gwamnatin jihar ta tabbatar dukkan matakan kula da barkewar cutar suna aiki don dakile yaduwarta a cikin kankanin lokaci,” inji Nwogwugwu.

Hukumar Yaki da Yaduwar Cututtuka ta Najeriya (NCDC) ta ce kawo yanzu mutum 172 ne aka tabbatar sun kamu da cutar a fadin kasa a 2022, sannan cutar ta kashe mutum hudu.