✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Mutum miliyan 13 na fuskantar barazanar yunwa a Afirka – MDD

Hukumar ta ce hakan ya faru ne sakamakon karancin ruwan sama.

Hukumar Kula da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya (WFP), ta yi gargadin cewa akwai kimanin mutum miliyan 13 da ke fuskantar barazanar tsananin yunwa saboda farin da aka fuskanta a sassa da dama na nahiyar Afirka.

Hukumar dai ta ce farin da aka fuskanta sakamakon karancin ruwan sama da aka fuskanta a shekara uku a jere na matukar barzana ga nahiyar.

A cikin wata sanarwa da Daraktan hukumar da ke Gabashin Afirka, Michael Dunford ya fitar ranar Talata, hukumar  ta ce, “Karancin ruwan ya kawo cikas a bangarori da dama, dabbobi na mutuwa, yunwa na karuwa sannan fari na dada kunno kai.

“Lamarin na bukatar a kawo daukin gaggawa da kuma kai tallafi a kai a kai don taimaka wa iyalai da dama.”

Daukewar ruwan sama kafin lokacin da aka saba gani a kasashen Afirka da dama dai da kuma tashin farashin gwauron zabin da kayan abinci da na sauran masarufi ke yi da kuma raguwar bukatar mutane su yi aiki a gonaki ya dada ta’azzara matsalar.

WPF dai ta ce barazanar na tilasta wa iyalai da dama yin kaura zuwa wasu yankunan, inda ta yi barazanar karuwar rikice-rikice in ba a kai wa mutane dauki ba.

Hukumar dai ta sha yin gargadi kan barazanar farin da kuma yiwuwar uskantar matsalar yunwa, wadanda za su iya rura wutar rikici a yankunan nahiyar da ma wasu sassa na nahiyar Asia.