✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Mutum Miliyan 25 Ke Dauke Da Cutar AIDS A Afirka —WHO

Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta ce nahiyar Afirka ce ta fi yawan masu dauke da cuta mai karya garkuwar jiki (AIDS) a duniya.

Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta ce nahiyar Afirka ce ta fi yawan masu dauke da cuta mai karya garkuwar jiki (AIDS) a duniya.

Daraktar Shiyya na Hukumar reshen Afirka, Dokta Matshidiso Moeti ce ta bayyana hakan a sakonta na ranar tunawa da masu dauke da cutar ta bana, inda ta ce mutane miliyan 25.6 ne ke dauke da cutar a nahiyar.

Dokta Matshidiso ta ce duk da yawan adadin, an samu raguwar masu cutar a yankin da kaso 44 cikin 100,  idan aka kwatanta da shekaru 10 na baya.

“A sauran larurorin ma da ke da alaka da cutar an samu saukinsu da kashi 55 a shekarun sakamakon kokarin WHO da kawayenta, wajen wayar da kan al’umma da bada tallafi da fadada sabbin dabarun kau da cutar, hadi da samar da na’u’rorin dakile ta,” in ji ta.

Sauran abubuwan da suka taimaka a cewarta sun hada da samun karin magunguna masu arha, wuraren gwaji da kayan aiki da ma tallafi da yankin Arewa maso Yamma da Afirka ta Tsakiya ke samu.

Ana gudanar da bikin ne a duk ranar 1 ga watan Disamba domin jawo hankalin duniya game da cutar, da tunatar da masu ruwa da tsaki cewa har yanzu tana nan a duniya.