✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Na san yadda zan farfado da tattalin arzikin Najeriya —Tinubu

Tinubu ya ce ya fi sauran 'yan takara sanin makamar aiki da kwarewa.

Dan takarar Shugaban Kasa na jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu, ya ce ya san yadda zai farfado da tattalin arzikin Najeriya fiye da sauran abokan karawarsa a zaben da ke tafe.

Ya bayyana haka ne a ranar Laraba a Lokoja, babban birnin Jihar Kogi, a lokacin yakin neman zabensa.

Tinubu ya ce, “Na san yadda zan yi. Na san yadda zan yi fiye da sauran ‘yan takara. Ni mutum ne da ya san hanya. Mutum ne da ya san yadda zai samar wa kasa kudi. Mutumin da yake cika alkawari,” a cewarsa.

Ya ce mutane da yawa sun nuna damuwa kan yadda ya yi korafi game da sabon tsarin canjin kudi, inda ya ce ya zuwa yanzu za a bar komai a hannun kotun koli har zuwa lokacin da za ta yanke hukunci.

Tinubu, akwai jihohi da dama da suke da albarkatun kasa, zai taimaka musu wajen gano su tare da cin moriyarsu.

Kazalika, ya ce zai farfado da kamfanin sarrafa man fetur na Ajaokuta da fadada kogin Neja sannan zai tada kamfononi da suka durkushe tare da inganta harkar noma da samar da ayyukan yi.

A nasa jawabin, Gwamna Yahaya Bello na Jihar Kogi, ya bayyana Tinubu a matsayin mutum mai tarin basira.

Bello ya kara da cewar idan Tinubu ya dare karagar mulkin Najeriya, “Zai farfado da kamfanin sarrafa karafa na Ajaokuta. Matsalar rashin tsaro da ta addabi kasar nan ma zai magance ta,” in ji shi.