✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

NAJERIYA A YAU: Yadda harkar Kudi ta intanet ta Sa ’yan Najeriya tafka asara

Rashin karfin intanet na wahalar da ’yan Najeriya wajen yin hada-hadar kudi

More Podcasts

Domin saukewa latsa nan.

’Yan Najeriya na kokawa kan rashin tabbas da kuma wahalar da suke sha wajen yin hada-hadar kudi ta intanet.

Yawanci a Najeriya idan mutum zai tura kudi ta intanet yakan kasance cikin fargaba — ko kudin ya ki tafiya, ko kuma ya tafi daga wurinsa, amma ya makale a hanya, ya ki zuwa inda aka tura.

Shin me ya sa ake yawan samun matsalar harkar kudi ta intanet a Najeriya? Ina mafita?

Shirin Najeriya A Yau ya tattauna da ’yan Najeriya da masana a kan wannan al’amari.