More Podcasts
A karshen makon da ya gabata ne sojojin Najeriya suka shiga wani kauye suka a ragargaji gungun wasu ’yan ta’adda da suka mayar da kauyen sansaninsu.
Rahotanni sun tabbatar cewa babu mutumin kirki ko daya da ya rage a kauyen bayan ’yan ta’adda sun tare a cikinsa.
- DAGA LARABA: Kamen ’Yan Arewa: Shin Lokacin Daina Ci-Rani Ya Yi
- NAJERIYA A YAU: Yadda Kwadayi Ya Kai ’Yan Najeriya Tashar Wulakanci A Aljeriya
A shirinmu na yau mun tattauna da makwabtan kauyen da ke Karamar Hukumar Chikun ta Jihar Kaduna; sun kuma ba mu cikakken labarin irin namijin kokarin da sojojin suka yi a wannan karon.
Domin sauke shirin domin sauraro a duk lokacin da ku ke so latsa nan