✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

NATO na kokarin hana China fadada karfin nukiliyarta

NATO na kokarin dakile yunkurin China na fadada nukiliyarta.

Kungiyar Tsaro ta NATO ta bukaci kasar China ta shiga cikin tattaunawar kayyade yawan makaman da kowace kasa za ta iya mallaka a wani kokari na dakile yunkurin kasar na fadada nukiliyarta.

Babban Sakataren Kungiyar NATO, Mista Jens Stoltenberg ya nuna damuwa kan yadda China take ci gaba da fadada makamashinta na nukiliya.

A cewarsa, akwai bukatar kasar ta mutunta dokokin duniya wajen shiga tattaunawar kayyade yawan makaman don kauce wa hadarin da matakin nata kan iya haifarwa.

Stoltenberg a ganawarsa da Ministan Harkokin Wajen China, Mista Wang Yi, ta bidiyo, ya ce duk da kasancewar China ba ta cikin mambobin NATO amma yana da kyau ta mutunta dokokin duniya.

A zantawar tasu Stoltenberg ya ce akwai bukatar China ta rika bayyana wa duniya irin makaman da take mallaka ba tare da nuku-nuku ba.

Kuma ya kamata a ce ayyukanta na soji a fili take yin su sabanin yadda take boyewa.

China dai tana cikin kasashen da suke da karfin makamin nukiliya a duniya, sai dai NATO tana nuna fargaba a lokuta da dama game da rashin fayyace wa duniya matakin da ta kai a bangaren nukiliya.