✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

NCC ba ta da shirin rufe hanyoyin sadarwa a Katsina – Gwamnati

Gwamnatin Katsina ta bayyana labarin a matsayin na kanzon kurege.

Hukumar Kula da Kafofin Sadarwa ta Kasa (NCC) ta musanta labaran da ke yawo a kafafen sada zumunta cewa ta ba kamfanonin sadarwa umarnin toshe hanyoyin sadarwa a Jihar Katsina.

Daraktan Yada Labarai na Gwamna Aminu Bello Masari, Alhaji Abdul Labaran ne ya tabbatar da hakan a cikin wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a Katsina ranar Litinin.

Ya ce Shugaban Hukumar ta NCC, Farfesa Umar Garba Danbatta wanda ya yi magana da Gwamnatin Jihar ya bayyana labarin a matsayin na kanzon kurege.

“Danbatta ya kuma ce takardar wacce take yawo a kafafen sada zumunta na zamani an jirkita wacce suka fitar a kan Jihar Zamfara ce a makon jiya,” inji shi.

Daga nan sai Alhaji Labaran ya shawarci jama’a da su yi watsi da labarin a matsayin wanda ba shi da tushe ballantana makama kasancewar ba daga NCC ya fito ba.

Idan za a iya tunawa, NCC a makon da ya gabata ta umarci dukkan kamfanonin sadarwa su katse dukkan hanyoyin sadarwa a Jihar Zamfara a matsayin daya daga cikin irin matakan da ake dauka wajen yaki da ayyukan ’yan bindiga a Jihar.