✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

NDLEA ta kama kulli 20 na Hodar Iblis da aka boye a kwalayen sabulu

NDLEA ta ce an kama kwayoyin ne da ake shirin kai su Landan daga Legas.

Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi ta Kasa (NDLEA) ta kama kulli 20 na Hodar Iblis da Tabar Wiwi da ake shirin tafiya da su Landan a filin jirgin saman Murtala Muhammad da ke Legas.

Kakakin hukumar, Femi Babafemi ne ya sanar da hakan a cikin wata sanarwa ranar Lahadi.

Ya ce an kama kwayoyin ne yayin wani binciken jirgin daukar kaya da Kamfanin Harkokin Sufurin Jiragen Sama na Najeriya (NAHCO) suka yi a filin.

Babafemi ya ce kullin da aka kama ya kai nauyin kilogiram 1.2 kuma an kunshe su ne a cikin kwalayen sabulu.

Kakakin ya kuma ce jami’an hukumar sun kama wasu kulli 23 na Tabar Wiwi mai nauyin kilogiram 1.4 da aka boye a kwalin sabulu, da kulli 39 na kwayar Methamphetamine wacce ita kuma aka boye a kwalin sabulun Dudu Osun.

Sanarwar ta ce tuni aka cafke mutum uku da ake zargi da hannu a kayan da aka kama.

Babafemi ya kuma ce, “Mun kama wata uwa mai shayarwa mai suna Mariam Dirisu wacce tai ikirarin zama dalibar aji hudu a Jami’ar Benin, ita ma da muka kama kan safarar kwayoyi.

“Dubunta ta cika ne kasa da mako daya bayan an bayar da belinta lokacin da aka kama ta tana kokarin safarar kwayoyi a cikin garin rogo ga wani wanda yake tsare a hannun NDLEA.

“Jami’an hukumarmu a Jihar Edo ne dai suka fara kama matar, mai kimanin shekara 35 a ranar 21 ga watan Oktoban 2021,” inji Babafemi.

Kakakin dai ya ce tuni Shugaban hukumar, Brigediya Janar Buba Marwa (mai ritaya) ya bayar da umarnin a ja kunnen matar sannan a gaggauta sakinta saboda yarinyar da take shayarwa.